Makamai 40 da Iran Ta Harba Sun Gamu da Cikas, An Kakkaɓo Su kafin Su Kai Isra'ila
- Rundunar sojin Isra'ila ta yi ikirarin cewa dakarunta sun kakkaɓo jirage marasa matuƙa na bam da Iran ta harbo zuwa cikin ƙasarta
- A wata sanarwa da sojojin suka fitar, sun ce kawo yanzu Iran ta harbo makamai sama da 470 amma duk kusan ta yi nasarar kakkaɓo su
- Wannan dai na zuwa ne a lokacin da yaƙi tsakanin kasashen biyu ke kara ta'azzara a rana ta takwas watau yau Asabar
Ahmad Yusuf, kwararren edita ne a Legit Hausa da ya shafe tsawon shekaru yana kawo muku rahotannin siyasa, nishadi da al'amuran yau da kullum
Tel Aviv, Israel - Ƙasar Iran ta sake harba jirage marasa matuƙa masu fashewa kamar bam zuwa Isra'ila, sai dai hukumomi sun ce sun tare su ba tare da matsala ba.
Rundunar sojin Isra’ila ta ce dakarunta na sama sun kakkaɓo kusan jiragen sama marasa matuki guda 40 da aka harbo daga Iran cikin dare.

Asali: Twitter
A rahoton da Aljazeera ta kawo, rundunar ta yi ikirarin cewa ta samu nasara kusan kashi 99 cikin 100 na harbo irin waɗannan makaman tun da ta fara rikici da Iran.
LURA: Shin kana son bamu labari da tattaunawa da marubutanmu? Tuntubemu a [email protected]
Isra'ila ta yi ikirarin kakkabo makaman Iran
Wannan ikirari na rundunar sojin kasar Isra'ila na nuni da cewa mafi yawan makaman da Iran ta harbo, ba su kai ga wurin da aka nufi su ruguza ba.
A yau Asabar, 21 ga watan Yuni, 2025 aka shiga rana ta takwas tun bayan ɓarkewar rikici tsakanin ƙasashen biyu a ranar Juma'a, 13 ga watan Yuni.
A cikin wata sanarwa, rundunar sojin ta ce:
“A daren jiya Juma'a, sojojin sama sun yi nasarar harbo kimanin jirage marasa matuki guda 40 da aka turo daga Iran zuwa cikin ƙasar Isra’ila.”
“Wannan adadi na makaman da aka harbo na ci gaba da ƙaruwa tun daga farkon ranar da aka fara musayar wuta
"A yanzu alƙaluma sun nuna Iran ta harbo makamai fiye da 470 kan Isra'ila, amma dai sojojin mu na sama sun kakkaɓo kashi 99 cikin 100 na jirage marasa matuƙa.”

Asali: Getty Images
Sojojin Isra'ila sun kai hari wasu wurare a Iran
Sanarwar ta kuma bayyana cewa jiragen yaƙi na musamman na Isra'ila ƙarƙashin jagorancin ɓangaren leƙen asiri, sun kai farmaki kan wata na’urar harba makamai ta Iran a birnin Isfahan.
Bugu da ƙari, rundunar sojin Isra’ila ta bayyana cewa dakarunta suna kai farmaki kan cibiyoyin soji da ke Kudu maso Yammacin Iran.
Sojojin sun jaddada cewa za su ci gaba da ƙoƙarin kakkabo duk wani makamai ko jirgi da aka harbo, sannan ta maida martani mai zafi kan muhimman wurare a Iran.
Iran ta kara ɓarin wuta a Isra'ila
A wani labarin, kun ji cewa rahotanni sun nuna cewa Iran ta harba makamai masu linzami zuwa wasu sassan Isra’ila da sanyin safiyar ranar Asabar, 21 ga Yuni.
Daga cikin yankunan da Iran ta yi wa ɓarin wuta a Isra'ila a wannan rana har da unguwar Holon, inda aka hangi gobara da hayaki na tashi.
Sojojin Isra’ila sun bayyana cewa wannan rikicin na iya ɗaukar lokaci mai tsawo, la'akari da yadda ƙasashen biyu ke kallon juna a matsayin abokan gaba.
Wanda ya tantance Muhammad Malumfashi, babban edita a Legit.ng.
Asali: Legit.ng